IQNA

Hankoron Sake Mayar Da Hannun Agogo Baya Ta Fuskar Mulki A Yammacin Afirka

23:53 - February 14, 2022
Lambar Labari: 3486949
Tehran (IQNA) Hamɓarar da Shugaba Kaboré shi ne juyin mulki na huɗu a Afirka ta Yamma cikin watanni 17 da suka gabata.

Ita kuwa ƙasar Mali, ta fuskanci juyin mulkin ne har sau biyu cikin wannan lokacin saboda zargin da ake yin a cewa gwamnati ta kasa kawo ƙarshen yaƙin masu iƙirarin jihadi da suka addabi kasar.

A kasar Burkina Faso ma, sauke Kabore ya biyo bayan zargin da wasu sojoji suka yi cewa gwamnatinsa ba ta ba su goyon bayan da ya dace wajen yaƙi da 'yan bindiga masu iƙirarin jihadi da ke da alaƙ da ƙungiyoyin al-Qaeda da Islamic State.

A ranar Lahadi an samu rahotannin yin bore a barikokin sojoji da dama a babban birnin ƙasar Ouagadougou, da kuma garuruwan Kaya da Ouahigouya.

Rikcin ya biyo bayan watanni da aka shafe ne ana yi wa gwamnati bore da zimmar neman shugaban ƙasa ya sauka daga mulki.

Rikicin 'yan bindigar da ya fara a 2015 ya kashe aƙalla mutum 2,000 sannan ya raba miliyan ɗaya da rabi da gidajensu, a cewar an rufe makarantu a sassan ƙasar da yawa saboda abu ne mai haɗari ga ɗalibai.

An yanke ƙauna kan shugaban ƙasar ne jim kaɗan bayan an kai hari kan garin Solhan da ke arewacin ƙasar a watan Yunin 2021. Fiye da mutum 100 ne suka mutu a harin da aka zargi 'yan bindigar da suka tsallako daga Mali da aiwatar da shi.

Harin ya jawo zanga-zanga a faɗin ƙasar, lamarin da yasa Shugaba Kabore ya yi wa gwamnatinsa garambawul, inda ya naɗa kansa a matsayin ministan tsaron kasar ta Burkina Faso.

Haka nan kuma  wani harin da aka kai kan sansanin soja na Inata a watan Nuwamban 2021 ya ƙara ta'azzara fushin al'umma a kan gwamnati.

Jami'an tsaro fiye da 50 aka kashe. Daga baya an samu rahoto cewa dakarun sansanin sun nemi a kawo musu kayan abinci da kuma kayan aiki sati biyu kafin harin, amma babu su babu labarinsu.

Shugaban ya kori dukkan ministocinsa, ya naɗa sabon firaminista da kuma ministan tsaro yayin da ake shirin tattaunawa da 'yan jam'iyyar adawa.

Duk da matsalolin tsaro da na siyasa da ake fama da su a Afirka ta Yamma, Burkina Faso ba ta daga cikin kasashen da suke fuskantar irin wadannan matsaloli na tsaro, musamamn na masu da’awar jihadi, har zuwa boren da aka yi a 2014, wanda ya haddasa kifar da gwamnatin Blaise Compaoré - shugaban da ya fi kowa daɗewa a kan mulki.

Wani yunƙurin juyin mulki da aka yi a 2015 ya raba kan sojojin sosai. An zaɓi Mista Kabore a wannan shekarar da zimmar zai haɗa kan ƙasar.

Sai dai kuma 'yan bindiga daga Mali - inda masu iƙirarin jihadi suka yi nasarar ƙwace fafutukar ɓallewa a 2012 - sun kai hari a babban birnin ƙasar a lokacin da Mista Kabore ke shirin hawa mulki.

'Yan bindigar sun yi amfani da damar da suka samu ta ƙarancin kayan aiki na jami'an tsaro wajen kai hare-hare a kan iyaka, sannan suka kafa kansu a cikin wadannan yankunan.

Masu jihadin sun haddasa husuma tsakanin Musulmai da Kiristoci da suka daɗe suna zaman lafiya da juna a baya a kasar Burkian Faso.

Kazalika, sun yi amfani da irin halin ƙuncin rayuwa da mutane suke ciki na rashin tallafin gwamnati.

A 2020, mutanen da suka tsere daga gidajensu ba su samu damar jefa ƙuri'unsu ba a zaɓen shugaban ƙasar, wanda Mista Kabore ya yi nasara da kashi 58 cikin 100 a wa'adi na biyu.

An yi ta samun fargaba cewa wani sabon tsari na shirin faruwa.

Abubuwan da suka faru kafin juyin mulkin sun yi kama da waɗanda suka faru a Mali kafin a hamɓarar da gwamnati a watan Agustan 2020.

Mutane sun fara zanga-zanga ne bayan hare-haren da aka dinga kai wa kan sojoji da mutanen gari, abin da ya sa 'yan ƙasa suka yanke ƙauna da gwamnatin Mali ta Marigayi Ibrahim Boubacar Keïta.

Sai dai kuma yayin da 'yan Mali suka goyi bayan juyin mulkin, 'yan Burkina Faso za su kasance cikin ɗar-ɗar saboda kar abin da ke faruwa ya ci gaba a ƙarƙashin mulkin soja.

Dukkan ƙasashen sun kasance ƙarƙashin mulkin mallakar Faransa kuma ƙasar ta ci gaba da ƙawancen soja da na tattalin arziki masu girma a ƙasashen har bayan da suka samu 'yancin kansu.

Kamar dai yadda lamarin yake a Mali, sojojin Burkina sun dogara da tallafin da Faransa ke ba su wadda ta tura sojoji 5,100 a yankin cikin wani shiri da ta kira Operation Barkhane.

An ƙaddamar da shirin ne lokacin da Faransa ta tura sojoji su dakatar da masu iƙirarin jihadi shiga babban birnin Mali Bamako a 2013.

Sai dai 'yan ƙasa sun fara dawowa daga rakiyar Faransa bayan abubuwa sun ƙara taɓarɓarewa.

A watan Disamban 2021, wasu mazauna Kauye sun tare wa dakarun Faransa hanya da ke kai wa sojojin Burkina kaya suna masu zargin dakarun na Faransa da haɗa baki da masu iƙirarin jihadi.

An ci gaba da korar Faransa daga yankin na Sahel sakamakon hatsaniya tsakaninta da Mali, abin da ya sa Faransa ta janye kusan rabin sojojinta.

'Yan bindigar ka iya yin amfani da giɓin da aka samu, yayin da rikicin siyasar da ya ƙi ci ya ƙi cinyewa ka iya haifar da rashin yin aiki tare tsakanin sojojin haɗin gwiwa na G5 Sahel, wanda ya ƙunshi dakarun Mali da Nijar da Burkina Faso da Chadi da kuma Mauritania.

A lokacin da Mali ke neman taimakon Rasha domin magance matsalar tsaro, maƙwabtanta na Sahel - kamar Burkina Faso - ba sa goyon bayan wannan shiri ko kaɗan.

Juyin mulki a Burkina Faso na nuna cewa masu aikata shi ba sa tsoron matakan da ƙungiyar Ecowas - ta ƙasashen Afirka ta Yamma - za ta ɗauka a kan su. Takunkuman da aka saka wa Mali da Guinea a kwanan nan bai hana sojoji ci gaba da aiwatar da juyin mulki  ba.

Shi ma Shugaba Mohamed Bazoum na Nijar ya fara mulki cikin fargaba a 2021 lokacin da aka yi yunƙurin juyin mulki a ƙasar kafin a rantsar da shi.

Ya sha sukar rikicin siyasar da ke faruwa a maƙwabciyar Jamhuriyar Nijar wato Mali, da kuma tasirin da hakan zai yi kan dakarunsu a yaƙi da masu iƙirarin jihadi.

Shugaban na yunƙurin kauce wa duk wata fargaba da za a nuna game da harkokin tsaro ta hanyar ziyartar dakaru a fagen fama, wanda yasa ake ganin suna aiki.

Tashin hankalin da ke faruwa a Mali da Burkina na ƙoƙarin shafar maƙwabciyarsu Ivory Coast, inda aka samu hare-haren masu iƙirarin jihadi a yankunan ƙasar tun daga Yunin 2020, da ake kai wa jami'an tsaro a kasar.

A halin yanzu dai kallo ya koma ga sojojin kasar ta Burkina faso domin ganin kamun ludayinsu bayan hambarar da shugaba Kabore, da kuma irin rawar da za su iya takawa musammana  bangaren ayyukan tabbatar da tsaro, wanda shi ne yafi ci ma jama’a tuwo a kwarya a kasar.

Abubuwan Da Ya Shafa: addabi burkina faso
captcha